1 Samuel 2:30 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Saboda haka Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na yi alkawari cewa gidanka da gidan mahaifinka za su yi mini hidima a gabana har abada.’ Amma, yanzu Allah ya ce, ba zai yiwu ba; waɗanda suke girmama ni; Ni ma zan girmama su. Amma waɗanda suke ƙasƙantar da ni, haka za a ƙasƙantar da su.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«سَبُواْدَ حَكَ، يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ يَثٜىٰ، ‹كُواْدَيَكٜىٰ نَيِ أَلْڧَوَرِ دَكَيْ دَ غِدَنْ مَحَيْڢِنْكَ ثٜىٰوَ ذَاكُيِ مِنِ حِدِمَ حَرْ أَبَدَا، عَمَّا يَنْذُ، إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ، كُواْ كَطَنْ وَنَّنْ بَذَيْ يِوُ كُمَ بَ! غَمَا نَكَنْ غِرْمَمَ وَطَنْدَ سُكٜىٰ غِرْمَمَ نِے، عَمَّا وَطَنْدَ سُكٜىٰ رٜىٰنَ نِے ذَاسُ شَا وُلَڧَنْثِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ni Ubangiji Allah na Isra'ila, na yi alkawari a dā cewa, ‘Kai da iyalinka da danginka za ku yi mini aikin firist har abada.’ Amma yanzu na ce ba zan yarda da wannan ba. Waɗanda suke girmama ni, zan girmama su. Waɗanda suke raina ni zan ƙasƙantar da su ƙwarai.