1 Samuel 20:12 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Yonatan ya ce wa Dawuda, “Na yi rantse da Ubangiji, Allah na Isra’ila cewa war haka jibi, zan yi ƙoƙari in ji daga mahaifina, idan ya yi magana mai kyau game da kai, zan gaya maka.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يُواْنَتَنْ يَثٜىٰ «نَا ضَنْڟٜىٰ مَكَ دَ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ؞ جِيبِے دَيْدَيْ وَنَّنْ لُواْكَثِ ذَنْيِ ڧُواْڧَرِ إِنْسَنْ كُواْ مٜىٰنٜىٰنٜىٰ تُنَانِنْ بَابَنَ غَمٜىٰدَ كَيْ؞ عِدَنْ بَاشِ دَمُوغُنْ نُڢِ غَمٜىٰدَ كَيْ ذَنْعَيْكَ مَكَ كَجِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan Jonatan ya ce wa Dawuda, “Ubangiji Allah na Isra'ila zai zama shaida. Gobe war haka, ko jibi zan tattauna maganar da mahaifina, idan da nufin alheri zuwa gare ka, zan aika, in faɗa maka.