1 Samuel 21:1 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Dawuda ya tafi Nob a wurin Ahimelek firist. Da Ahimelek ya gan shi sai ya firgita ya ce, “Me ya sa kai kaɗai ne? Me ya sa ba wani tare da kai?”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَاوُدَ يَتَڢِے وُرِنْ أَهِمٜىٰلٜىٰكْ وَنْدَ يَكٜىٰ ڢِرِسْتِ أَغَرِنْ نُوابْ؞ أَهِمٜىٰلٜىٰكْ يَيِ ضَوَرْ جِكِے سُواْسَيْ دَ يَغَ دَاوُدَ، سَيْ يَتَمْبَيٜىٰشِ يَثٜىٰ «يَيَ كَكٜىٰ كَيْ كَطَيْ؟ كُمَ يَيَ بَابُ كُواْوَ تَرٜىٰدَكَيْ؟»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan Dawuda ya tafi wurin Ahimelek, firist, a Nob. Ahimelek kuwa ya fita da rawar jiki domin ya tarye Dawuda, ya ce masa, “Me ya sa kake kai kaɗai, ba wani tare da kai ba?”