1 Samuel 22:7 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya ce musu, “Mutanen Benyamin, ku saurara; ɗan Yesse zai iya ba dukanku filaye da gonakin inabi ne? Zai ba dukanku shugabanci na dubbai ko shugabanci na ɗari-ɗari?
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ طَالُوتَ يَثٜىٰ وَمَاسُ يِمَسَ حِدِمَ «كُسَوْرَرَتَ مُتَنٜىٰنْ بِلِيَامِنُ! كُنَ ڟَمَّنِ دَاوُدَ طَنْ يٜىٰسّٜىٰ ذَيْ عِيَ بَا دُكَنْكُ ڢِيلَيٜىٰ دَ غُواْنَكِنْ إِنَبِے نٜىٰ؟ يَكُمَ مَيْدَكُو شُوغَبَنِّنْ سُواْجُواْجِنْ دُبُو دُبُو دَ كُمَ نَطَرِے طَرِے نٜىٰ؟
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai ya ce wa fādawan da suke tsaye kewaye da shi, “Ku ji, ya ku mutanen Biliyaminu, ɗan Yesse zai ba kowannenku gonaki, da gonakin inabi ne? Zai maishe ku shugabanni na dubu dubu, da na ɗari ɗari, har da dukanku kuka yi mini maƙarƙashiya? Ba wanda ya sanar da ni sa'ad da ɗana ya haɗa kai da ɗan Yesse? Ba wanda ya damu saboda da ni, balle a faɗa mini yadda ɗana ya kuta barana ya tayar mini, yana fakona, kamar yadda yake a yau?”