1 Samuel 23:5 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Dawuda da mutanensa suka tafi Keyila, suka yi yaƙi da Filistiyawa, suka kwashe musu shanunsu, suka jijji wa Filistiyawa ƙwarai, suka cece mutanen Keyila daga hannunsu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ دَاوُدَ دَ مُتَنٜىٰنْسَ سُكَ تَڢِے كَيْلَ سُكَيِ يَاڧِ دَ ڢِلِسْتِيَاوَا؞ سُكَ كَكَّشٜىٰسُ دَيَوَ سُكَ ڨُوثٜىٰ دَبُّواْبِنْسُ؞ تَهَكَنٜىٰ دَاوُدَ يَثٜىٰثِ مَذَوْنَنْ غَرِنْ كَيْلَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan Dawuda da mutanensa suka tafi Kaila, suka yi yaƙi da Filistiyawa, suka kashe su da yawa, suka kwashe shanunsu. Da haka Dawuda ya kuɓutar da mazaunan Kaila.