1 Samuel 25:39 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Da Dawuda ya sami labarin mutuwar Nabal, sai ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya sāka mini a kan irin renin da Nabal ya yi mini. Ya hana bawansa yin mugunta, ga shi ya ɗora wa Nabal muguntar da ya yi.” Sai Dawuda ya aika wa Abigiyel cewa tă zama matarsa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ دَاوُدَ يَجِ نَبَلْ يَمُتُ، سَيْيَثٜىٰ «أَلْبَرْكَ تَا تَبَّتَا غَ يَهْوٜىٰهْ ، وَنْدَ يَڟَيَ مِنِ لُواْكَثِنْ دَ نَبَلْ يَكُنْيَتَرْ دَنِے؞ يَهْوٜىٰهْ يَا كُمَ هَنَنِ يِنْ مُغُنْتَا، يَكُمَ جُويَا مُغُنْتَارْ نَبَلْ عَكَنْسَ؞» سَعَنً دَاوُدَ يَعَيْكَ وَ أَبِغِيٜىٰلْ دَ سَڧُواْ ثٜىٰوَ يَنَ نٜىٰمَنْتَ دَ عَوْرٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'ad da Dawuda ya ji Nabal ya mutu, sai ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji wanda ya sāka mini a kan irin rainin da Nabal ya yi mini. Ya kuma hana ni aikata mugunta. Ya ɗora wa Nabal muguntarsa a kansa.” Sa'an nan Dawuda ya aika, ya nemi Abigail ta zama matarsa.