1 Samuel 28:15 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Don me ka dame ni, ta wurin hauro da ni?” Shawulu ya ce, “Ina cikin babban damuwa ce, Filistiyawa sun fāɗa mini, Allah kuma ya juya mini baya. Bai amsa mini, ko ta mafarki, ko kuma ta annabawa ba, saboda haka na kira ka don ka gaya mini abin yi.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَمَٰعِيلَ يَتَمْبَيِ طَالُوتَ يَثٜىٰ «دُوانْمٜىٰ كَدَمٜىٰنِ تَوُرِنْ تَادَنِ حَكَ؟» طَالُوتَ يَثٜىٰ «إِنَ ثِكٜىٰ دَ دَامُوَ ڨُورَيْ! ڢِلِسْتِيَاوَا سُنَ يَاڧِ دَنِے، كُمَ اللَّهْ يَرَبُ دَنِے؞ بَايَ أَمْسَ مِنِ كُواْمٜىٰ يَنْذُ، كُواْ تَوُرِنْ وَنِ أَنَّبِے، كُواْ تَوُرِنْ مَڢَرْكَيْ؞ دُواْمِنْ حَكَ نَكِرَاكَ كَڢَطَا مِنِ إِنْسَنْ أَبِنْدَ ذَنْيِ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Sama'ila ya ce wa Saul, “Don me ka dame ni, ka hawar da ni?” Saul ya ce, “Ina cikin babbar wahala, gama Filistiyawa suna yaƙi da ni, Allah kuma ya rabu da ni, ya ƙi amsa mini ko ta wurin annabawa ko ta mafarkai, saboda haka na kira ka, ka faɗa mini abin da zan yi.”