1 Samuel 5:10 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai suka aika da akwatin alkawarin Allah zuwa Ekron. Yayinda akwatin alkawarin Allah yana shiga cikin Ekron, mutanen Ekron suka yi ihu, suka ce, “An kawo mana akwatin alkawarin Allah na Isra’ila domin yă kashe mu da mutanenmu.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَبُواْدَ حَكَ سُكَ عَيْكَ دَ عَݣُوتِنْ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَ ذُوَا عٜىٰكْرُوانْ، وَنِ بِرْنِنْ ڢِلِسْتِيَاوَا؞ سَعَدَّ عَݣُوتِنْ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَ يَ إِسُواْ عٜىٰكْرُوانْ سَيْ مُتَنٜىٰنْ سُكَ ڢَشٜىٰ دَ كُوكَا سُنَ ثٜىٰوَ «أَنْ كَٰوُاْ عَݣُوتِ نَ اللَّهْ‌نْ إِسْرَٰٓءِيلَ دُواْمِنْ يَكَشٜىٰمُ دَ عِيَلَنْمُ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai suka kai akwatin alkawarin Allah zuwa Ekron. Amma da aka kai shi Ekron, sai mutanen Ekron suka fashe da kuka, suka ce, “Sun kawo mana akwatin alkawarin Allah na Isra'ila don ya kashe dukanmu.”