1 Samuel 6:19 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma Allah ya kashe waɗansu mutum saba’in na mutanen Bet-Shemesh domin sun leƙa cikin akwatin alkawarin Ubangiji. Mutane kuwa suka yi makoki domin Ubangiji ya hallaka mutane da yawa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَنَانً سَيْ وَطَنْسُ مُتَنٜىٰنْ بٜىٰتْ شٜىٰمٜىٰشْ سُنْ دُوبِے ثِكِنْ عَݣُوتِنْ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَ نَ يَهْوٜىٰهْ ؞ سَيْ يَهْوٜىٰهْ يَكَشٜىٰ مُتُمْ سَبَعِنْ عَثِكِنْسُ؞ مُتَنٜىٰنْ كُوَ سُكَيِ بَڧِنْ ثِكِ سُواْسَيْ سَبُواْدَ يَهْوٜىٰهْ يَا كَشٜىٰ مُتَنٜىٰ دَيَوَ عَثِكِنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Ubangiji ya kashe mutum saba'in daga cikin mutanen Bet-shemesh domin sun leƙa cikin akwatin alkawari na Ubangiji. Mutanen kuwa suka yi makoki ƙwarai domin Ubangiji ya kashe mutane da yawa daga cikinsu.