1 Thessalonians 2:4 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A maimako haka, muna magana ne kamar mutanen da Allah ya amince yă danƙa musu amanar wannan bishara. Ba ma ƙoƙari mu gamshi mutane sai dai Allah, mai auna zukatanmu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْدَيْ كَمَرْ يَدَّ اللَّهْ يَيَرْدَ دَمُو يَدَنْڧَ مَنَ أَمَانَرْ وَعَظِنْ لَابَرِ مَيْ دَاطِے، حَكَ مُكٜىٰ سَنَرْ دَشِ، بَدُواْمِنْ مُڢَرَنْتَا وَمُتَنٜىٰ رَيْبَ، سَيْدَيْ دُواْمِنْ مُڢَرَنْتَا وَ اللَّهْ رَيْ، وَنْدَ يَكٜىٰ ڠُودَ ذُوثِيَارْمُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
sai dai kamar yadda Allah ya yarda da mu, ya damƙa mana amanar bishara, haka muke sanar da ita, ba domin mu faranta wa mutane rai ba, sai dai domin mu faranta wa Allah, shi da yake jarraba zukatanmu.