2 Chronicles 12:5 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai annabi Shemahiya ya zo wurin Rehobowam da kuma wajen shugabannin Yahuda waɗanda suka taru a Urushalima don tsoron Shishak, ya kuma faɗa musu, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Kun yi biris da ni; saboda haka, yanzu na bashe ku ga Shishak.’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ أَنَّبِے شٜىٰمَيَ يَذُواْ وُرِنْ رٜىٰهُواْبُواْوَمْ دَ سَوْرَنْ شُوغَبَنِّنْ يَهُودَ وَطَنْدَ سُكَ تَارُ أَ عُرُوشَلِيمَ دُواْمِنْ سُنَ غُدُنْ شِشَكْ؞ يَثٜىٰ مُسُ «إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ، ‹كُنْ يَاشٜىٰنِ، دُواْمِنْ حَكَ نِے مَا إِنَ يَاشٜىٰكُ إِنَ بَاشٜىٰكُ أَ حَنُّنْ شِشَكْ؞› »
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai annabi Shemaiya ya zo wurin Rehobowam da sarakunan Yahuza waɗanda suka tattaru a Urushalima saboda Shishak, ya ce musu, “Ubangiji ya ce kun yashe shi, don haka shi ma ya bashe ku a hannun Shishak.”