2 Chronicles 15:8 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’ad da Asa ya ji waɗannan kalmomin da annabcin Azariya ɗan Oded annabi ya faɗa, sai ya sami ƙarfi hali. Ya kawar da gumaka masu banƙyama daga dukan ƙasar Yahuda da Benyamin da kuma daga garuruwan da ya ci da yaƙi a ƙasar tudu ta Efraim. Ya gyaggyara bagaden Ubangiji da yake a gaban shirayin haikalin Ubangiji.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَدَّ أَسَ يَجِ وَطَنَّنْ كَلْمُواْمِنْ يَهْوٜىٰهْ دَغَ أَنَّبِے أَظَرِيَ طَنْ عُواْدٜىٰدْ، سَيْ يَيِ ڧَرْڢِنْ ذُوثِيَا؞ يَكَوَرْدَ غُمَكَ مَاسُ ڧَظَنْتَادَغَ دُكَنْ ڧَسَرْ يَهُودَ دَ تَ بِلِيَامِنُ دَ كُمَ دَغَ غَرُرُوَنْدَ يَڨُوثٜىٰ عَيَنْكِنْ تُدَّيْ نَ إِڢْرَيِمْ؞ يَسَاكٜىٰ ڠَرَ بَغَدٜىٰنْ يَهْوٜىٰهْ وَنْدَ يَكٜىٰ أَغَبَنْ ذَوْرٜىٰنْ غِدَنْ يَهْوٜىٰهْ ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da Asa ya ji irin kalmomin da annabi Azariya ɗan Oded ya hurta, sai ya yi ƙarfin zuciya, ya kawar da gumakan nan masu banƙyama daga dukan ƙasar Yahuza da ta Biliyaminu, daga kuma biranen da ya ci a ƙasar tuddai na Ifraimu. Sa'an nan ya gyara bagaden Ubangiji wanda yake a ƙofar shirayin Haikalin Ubangiji.