2 Chronicles 16:14 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Suka binne shi a kabarin da ya fafe wa kansa a Birnin Dawuda. Suka sa shi a makara wadda aka rufe da kayan yaji da kuma turare dabam-dabam da aka niƙa, suka kuma ƙuna babbar wuta don girmama shi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَكَ بِنّٜىٰشِ ثِكِنْ كَبَرِنْدَ يَحَڧَ دَ كَنْسَ عَبِرْنِنْ دَاوُدَ، وَتُواْ عُرُوشَلِيمَ؞ عَكَ ݣُونْتَرْ دَشِ عَكَنْ وَنِ أَبِنْ ݣُونْثِيَرْدَ عَكَ ثِكَ دَ تُرَارٜىٰ دَ كَايَنْ ڧَنْشِ، سُكَ هُورَ بَبَّرْ وُتَا دُواْمِنْ سُغِرْمَمَشِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Aka binne shi a kabarin da shi da kansa ya haƙa a birnin Dawuda. Aka sa shi a makara wadda aka cika da kayan ƙanshi da na turare yadda gwanayen aikin turare suka shirya, suka hura babbar wuta don su darajanta shi.