2 Chronicles 16:6 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Sarki Asa ya kawo dukan mutanen Yahuda, suka kuma kwashe duwatsu da katako daga Rama waɗanda Ba’asha yake amfani da su. Da su ne Asa ya gina Geba da Mizfa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَنً سَرْكِے أَسَ يَتَتَّارَ دُكَنْ مُتَنٜىٰ دَغَ يَهُودَ، يَسَاسُ سُݣُوشِ دُووَڟُنْ دَ كَتَكَنْ دَ بَعَشَ يَيِ أَمْڢَانِ دَسُو يَغِنَ كَتَنْغَرْ رَمَ؞ أَسَ يَيِ أَمْڢَانِ دَ دُووَڟُنْ يَڠَغْڠَرَ كَتَنْغَرْ غَرُضُوً غٜىٰبَ دَ نَ مِظْڢَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan sarki Asa ya kawo dukan mutanen Yahuza, suka kwashe duwatsun da katakan da Ba'asha yake gina Rama da su, ya gina Geba da Mizfa da su.