2 Chronicles 19:10 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Cikin kowane batun da ya zo gabanku daga ’yan’uwanku waɗanda suke zama a birane, ko batun na kisa ne ko kuwa waɗansu batuttuwan da suka shafi doka, umarnai, ƙa’idodi ko farillai, dole ku ja musu kunne kada su yi wa Ubangiji zunubi; in ba haka ba fushinsa zai sauko a kanku da ’yan’uwanku. Ku yi wannan, ta haka ba za ku kuwa yi zunubi ba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مُتَنٜىٰنْ يَهُودَ ذَاسُ كَٰوُاْ مُكُ دَامُوَ إِرِ إِرِ دَغَ جَمَعَرْكُ وَطَنْدَ سُكٜىٰ ذَمَ أَوَطَنْسُ بِرَنٜىٰنْ ڧَسَرْ؞ مَيْ يِوُوَ دَامُوَرْ غَمٜىٰدَ ذَنْثٜىٰنْ ظُبْدَ جِنِ نٜىٰ، كُواْ كَرْيَ كُواْيَرْوَرْ مُوسَٰى، كُواْ عُمَرْنَيْ، كُواْ ڧَٰعِدُواْدِ، كُواْ دُواْكُواْكِ؞ دُكْ سَعَدَّ سُكَ كَٰوُاْ دَامُوَرْ، كُجَا مُسُ كُنّٜىٰ كَدَ سُجَٰوُاْ وَكَنْسُ لَيْڢِے أَغَبَنْ يَهْوٜىٰهْ ؞ عِدَنْ بَهَكَبَ، ڢُشِنْ يَهْوٜىٰهْ ذَيْذُواْ عَكَنْكُ دَ یَنْعُوَنْكُ؞ عِدَنْ كُنْيِ بِيَيَّ دَ وَنَّنْ، بَذَاكُ جَٰوُاْ وَكَنْكُ لَيْڢِے بَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A duk lokacin da 'yan'uwanku daga birane suka kawo muku maganar wata shari'a, wadda ta shafi zub da jini, ko karya shari'a, ko umarni, ko dokoki, ko farillai, sai ku koya musu, don kada su aikata laifi a gaban Ubangiji, don kada hasala ta same ku, ku da 'yan'uwanku. Abin da za ku yi ke nan, don kada ku yi laifi.