2 Chronicles 20:15 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya ce, “Saurara, Sarki Yehoshafat da dukan waɗanda suke zama a Yahuda da Urushalima! Ga abin da Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku ji tsoro ko ku fid da zuciya saboda wannan babbar runduna. Gama yaƙin ba naku ba ne, amma na Allah.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يَهَظِيٜىٰلْ يَثٜىٰ، «كُسَوْرَرَ دُكَنْكُ دَ دُكَنْ مُتَنٜىٰنْ يَهُودَ دَ مَذَوْنَنْ عُرُوشَلِيمَ دَ سَرْكِے يٜىٰهُواْشَڢَتْ؞ غَا أَبِنْدَ يَهْوٜىٰهْ يَڢَطَا مُكُ، ‹كَدَ كُجِڟُواْرُواْ، كُواْ كُڢِدَّ ذُوثِيَا دُواْمِنْ يَوَنْ سُواْجُواْجِنَّنْ دَ كُكٜىٰ غَنِ؞ غَمَا يَاڧِنْ بَنَكُ بَنٜىٰ، نَ يَهْوٜىٰهْ نٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Yahaziyel ya ce, “Ku ji, ku dukanku, mutanen Yahuza, da mazaunan Urushalima, da sarki Yehoshafat, ga abin da Ubangiji yake faɗa muku, ‘Kada ku ji tsoro, ko ku razana saboda wannan babban taro, gama wannan yaƙi ba naku ba ne, amma na Allah ne.