2 Chronicles 20:21 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Bayan suka yi shawara tare da shugabanni, sai ya zaɓi mutanen da za su ja gaban sojoji suna waƙa ga Ubangiji suna yabonsa saboda tsarkinsa suna cewa, “Ku yi godiya ga Ubangiji, gama ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَدَّ يَيِ شَوَرَا دَ جَمَعَ، سَيْ يَذَاٻِ مُتَنٜىٰنْ دَ ذَاسُ وُثٜىٰ غَبَنْ سُواْجُواْجِ سُتَادَ وَاڧَرْ يَبُواْ غَ يَهْوٜىٰهْ ، سُيَبٜىٰشِ سَبُواْدَ دَرَجَرْ ڟَرْكِنْسَ، سُنَ ثٜىٰوَ «كُيِ غُواْدِيَ غَ يَهْوٜىٰهْ ، غَمَا ڧَوْنَرْسَ مَرَرْ ثَنْجَاوَا تَهَرْ أَبَدَا ثٜىٰ!»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'ad da ya yi shawara da jama'a, sai ya zaɓi waɗanda za su raira waƙa ga Ubangiji, su yabe shi a natse sa'ad da suke tafe a gaban runduna, su ce, “Ku yi godiya ga Ubangiji, Saboda madawwamiyar ƙaunarsa Tabbatacciya ce har abada.”