2 Chronicles 20:6 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
ya ce, “Ya Ubangiji Allah na kakanninmu, ba kai ne Allah wanda yake sama ba? Kana mulki a bisa dukan mulkokin ƙasashe. Iko da girma suna a hannunka, kuma ba wanda zai iya tsayayya da kai.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يَتَادَ مُرْيَ ثِكِنْ أَدُّعَ يَثٜىٰ، «يَا يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نَكَاكَنِّنْمُ، بَ كَيْنٜىٰ اللَّهْ نَسَمَ بَ؟ بَ كَيْ كَكٜىٰ مُلْكِ عَكَنْ دُكَنْ مُلْكُواْكِنْ أَلْعُمَّنْ دُونِيَا بَ؟ إِيكُواْ دَ ڧَرْڢِے سُنَ أَ حَنُّنْكَ، كُمَ بَاوَنْدَ يَ إِسَ يَڢُسْكَنْثٜىٰكَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na kakanninmu, kai ne Allah na cikin Sama, kai ne kuma kake mulkin dukan al'umman duniya. A gare ka iko da ƙarfi suke, don haka ba wanda ya isa ya jā da kai.