2 Chronicles 24:20 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Ruhun Allah ya sauko a kan Zakariya ɗan Yehohiyada firist. Ya tsaya a gaban mutane ya ce, “Ga abin da Allah ya ce, ‘Me ya sa ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji ba? Ba za ku yi nasara ba. Domin kun yashe Ubangiji, shi ma ya yashe ku.’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ رُوحٌ اللَّهْ يَايِ إِيكُواْ عَكَنْ زَكَرِيَّا طَنْ يٜىٰهُواْيِدَ ڢِرِسْتِ؞ يَڟَيَ أَغَبَنْ جَمَعَ يَثٜىٰ مُسُ «اللَّهْ يَثٜىٰ، ‹دُوانْمٜىٰ كُكٜىٰ ڧِنْ بِيَيَّ دَ عُمَرْنَنْ يَهْوٜىٰهْ ؟ تُواْ، بَذَاكُ عِيَ يَلْوَتَبَ؞ سَبُواْدَ كُنْ رَبُ دَ بِنْ يَهْوٜىٰهْ ، شِے مَا يَرَبُ دَكُو؞› »
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Ruhun Allah ya sauko wa Zakariya, ɗan Yehoyada, firist, ya tsaya a gaban jama'a ya yi magana da su, ya ce, “Ga abin da Allah ya ce, ‘Don me kuke ƙetare umarnan Ubangiji, har da za ku rasa albarka? Saboda kun rabu da bin Ubangiji, shi ma ya rabu da ku.’ ”