2 Chronicles 25:16 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Tun yana cikin magana, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Rufe mana baki! Me zai hana a kashe ka?” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَنَ ثِكِنْ مَغَنَ كٜىٰنَنْ، سَيْ أَمَظِيَ يَأَمْسَ مَسَ يَثٜىٰ «شِنْ، يَوْشٜىٰ مُكَ نَطَكَ مَيْبَا سَرْكِے شَوَرَا؟ كَرُڢٜىٰ بَاكِنْكَ كُواْ كُوَ عَكَشٜىٰكَ!» سَيْ أَنَّبِنْ يَدَيْنَ مَغَنَ، عَمَّا يَثٜىٰ «نَا سَنِ ثٜىٰوَ اللَّهْ يَيِ نِيَّ يَهَلَكَاكَ نٜىٰ، غَمَا كَا عَيْكَتَ وَنَّنْ، بَكَكُمَجِ شَوَرَاتَبَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yana magana ke nan, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Ka rufe baki! In kuwa ba haka ba in sa a kashe ka.” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”