2 Chronicles 25:23 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya kawo shi Urushalima ya farfasa katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, wani sashe mai tsawon ƙafa ɗari shida.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ سَرْكِے يُواْوَشْ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ يَكَامَ سَرْكِے أَمَظِيَ نَ يَهُودَ، طَنْ يُواْوَشْ، جِيكَنْ أَهَظِيَ، أَ بٜىٰتْ شٜىٰمٜىٰشْ؞ يَكَٰوُاْ أَمَظِيَ أَ عُرُوشَلِيمَ، يَرُشٜىٰ كَتَنْ‌غَرْ بِرْنِنْ دَغَ ڧُواْڢَرْ إِڢْرَيِمْ حَرْ ذُوَا ڧُواْڢَرْ ݣُونَ، مَيْ نِيسَنْ ڧَڢَا طَرِے شِدَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yehowash Sarkin Isra'ila, ya kama Amaziya Sarkin Yahuza ɗan Yowash, wato jikan Ahaziya, a Bet-shemesh, ya kawo shi Urushalima. Ya rushe garun Urushalima har tsawon kamu ɗari huɗu, tun daga Ƙofar Ifraimu har zuwa Ƙofar Kusurwa,