2 Chronicles 26:15 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A Urushalima ya yi na’urori da gwanaye suka sarrafa don amfani a hasumiyoyi da kuma a kusurwar kāriya don harbin kibiyoyi da jefan manyan duwatsu. Sunansa ya bazu ko’ina, gama ya sami taimako sosai har ya zama mai iko.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَثِكِنْ عُرُوشَلِيمَ كُوَ يَيِ نَعُرُواْرِ، وَطَنْدَ ڠُونَيٜىٰنْ مُتَنٜىٰنٜىٰ سُكَ ڧِرْڧِرُواْ؞ أَنْ سَا نَعُرُواْرِ عَكَنْ غِنٜىٰ غِنٜىٰ مَاسُ ڟَيِ دَ كَنْ ݣُونَرْ كَتَنْ‌غَ دُواْمِنْ أَ هَرْبَ كِبِيُواْيِ دَ مَنْيَنْ دُوَڟُو؞ تَهَكَ سُونَنْسَ يَبَظُو كُواْعِنَ، غَمَا يَيِ تَسَامُنْ تَيْمَكُواْ مَيْ يَوَ، حَرْ يَذَمَ مَيْ ڧَرْڢِے سُواْسَيْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A Urushalima ya yi na'urori waɗanda gwanayen mutane ne suka ƙago don a sa su a hasumiya, da kan kusurwoyi, don a harba kibau, da manyan duwatsu. Da haka sunansa ya bazu ko'ina, gama ya sami taimako mai banmamaki, har ya zama mai ƙarfin gaske.