2 Chronicles 26:21 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sarki Uzziya ya kasance da kuturta har ranar mutuwarsa. Ya zauna a gidan da aka ware, da kuturci, aka kuma ware shi daga haikalin Ubangiji. Yotam ɗansa ya lura da fadan ya kuma yi mulkin mutanen ƙasar.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَرْكِے عُزِّيَ يَكَسَنْثٜىٰ مَيْ ثُوتَرْ ڢَتَرْ جِكِے حَرْ مُتُوَرْسَ؞ عَكَ كُوَ وَارٜىٰشِ، أَنْرَبَ شِ دَ غِدَنْ يَهْوٜىٰهْ غَمَا شِے مَيْ ثُوتَرْ ڢَتَرْ جِكِے نٜىٰ؞ يُواْتَمْ طَنْسَ يَلُورَ دَ غِدَنْ سَرْكِے، يَنَ كُمَ مُلْكٍ مُتَنٜىٰنْ ڧَسَرْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ta haka sarki Azariya ya kuturce, har zuwa ranar mutuwarsa. Saboda kuturtarsa, ya zauna a keɓe a wani gida, gama an fisshe shi daga Haikalin Ubangiji. Yotam ɗansa shi ya shugabanci iyalin gidan sarki, yana kuma mulkin jama'ar ƙasa.