2 Chronicles 26:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya yi yaƙi da Filistiyawa ya kuma rushe katangar Gat, Yabne da kuma Ashdod. Sa’an nan ya sāke gina garuruwa kusa da Ashdod da sauran wurare a cikin Filistiyawa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَتَڢِے يَيِ يَاڧِ دَ ڢِلِسْتِيَاوَا يَرُرُّشٜىٰ كَتَنْ‌غَرْ بِرَنٜىٰنْ غَتْ دَ تَ يَبْنٜىٰ دَ تَ أَشْدُوادْ؞ يَغِغِّنَ غَرُرُوَ عَثِكِنْ يَنْكِنْ أَشْدُوادْ دَ وَطَنْسُ وُرَارٜىٰ أَ ڢِلِسْتِيَاوَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Azariya kuwa ya tafi ya yi yaƙi da Filistiyawa, ya rushe garun Gat, da na Yamniya, da na Ashdod. Ya giggina birane a ƙasar Ashdod, da waɗansu wurare na Filistiyawa.