2 Chronicles 28:15 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai mutanen da aka kira sunansu suka tashi, suka ɗauki kamammun, da ganimar, suka sa wa dukan waɗanda suke tsirara sutura. Suka sa musu sutura, suka ba su takalma, suka ba su abinci da abin sha, suka shafa musu mai. Suka hawar da dukan raunana a kan jakuna, suka kai su wurin ’yan’uwansu a Yeriko, wato, Birnin Itatuwan Dabino, sa’an nan suka koma Samariya.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
شُوغَبَنِّنَّنْ حُطُ وَطَنْدَ عَكَ كِرَا سُونَيٜىٰنْسُ سُكَتَاشِ سُكَ رَرَّبَ رِيغُنَنْ دَ سُواْجُواْجِ سُكَ ݣُوشٜىٰ، سُنْ مَيَرْ غَ مُتَنٜىٰنْ دَسُكٜىٰ ڟِرَرَ؞ سُكَ بَا مُتَنٜىٰنْ رِيغُنَ دَ تَاكَلْمَ دَ عَبِنْثِ دَ أَبِنْ شَا؞ سُكَ وَوَّنْكٜىٰ مُسُ ثِيوُانْسُ دَ مَنْ ظَيْتُنْ؞ سُكَسَا مَرَسَ ڧَرْڢِے عَثِكِنْسُ عَكَنْ جَاكُنَ، سُكَ كُواْمَرْ دَسُو يٜىٰرِكُواْ، وَتُواْ بِرْنِ مَيْ عِتَتُوَنْ دَبِينُواْ، عِنْدَ یَنْعُوَنْسُ سُكٜىٰ؞ سَعَنً سُكَ كُواْمَ سَمَرِيَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai mutanen da aka kira sunansu suka tashi, suka ɗauki kamammun, da ganimar, suka sa wa dukan waɗanda suke tsirara sutura. Suka sa musu sutura, suka ba su takalma, suka ba su abinci da abin sha, suka shafa musu mai. Suka hawar da dukan raunana a kan jakuna, suka kai su wurin 'yan'uwansu a Yariko, wato birnin itatuwan dabino, sa'an nan suka koma Samariya.