2 Chronicles 29:30 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sarki Hezekiya da fadawansa suka umarci Lawiyawa su yabi Ubangiji da kalmomin Dawuda da na Asaf mai duba. Saboda haka suka rera yabai da murna, suka sunkuyar da kawunansu suka yi sujada.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ سَرْكِے هٜىٰزٜىٰكِيَ دَ دَتَّاوَنْسَ سُكَ عُمَرْثِ لَوِيَاوَا سُيِ تَيَبُوانْ يَهْوٜىٰهْ دَ كَلْمُواْمِنْ دَاوُدَ دَ نَ أَسَڢْ مَيْ غَنِ؞ دَ مُرْنَ سُكَيِ وَاڧُواْڧِنْ يَبُواْ، سُكَ رُسُنَ ڧَسَا سُكَيِ وَ يَهْوٜىٰهْ سُجَّدَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai sarki Hezekiya tare da sarakunansa, suka faɗa wa Lawiyawa su yi ta raira yabo ga Ubangiji da kalmomin Dawuda, da na Asaf maigani. Da murna suka raira yabo, suka sunkuya suka yi sujada.