2 Chronicles 29:31 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Hezekiya ya ce, “Yanzu kun keɓe kanku ga Ubangiji. Ku zo ku kuma kawo hadayu da hadayun godiya zuwa ga haikalin Ubangiji.” Saboda haka taron suka kawo hadayu da hadayun godiya, da kuma dukan waɗanda suke da niyya suka kawo hadayun ƙonawa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
هٜىٰزٜىٰكِيَ كُوَ يَثٜىٰ «تُواْ دَيَكٜىٰ كُو مُتَنٜىٰنْ يَهُودَ كُنْ كٜىٰٻٜىٰ كَنْكُ غَ يَهْوٜىٰهْ ، سَيْ كُمَڟُواْ كُسَ كُكَٰوُاْ هَدَايُ دَ ݣَوْتَيْ نَنُونَ غُواْدِيَ أَ غِدَنْ يَهْوٜىٰهْ ؞» تَرُوانْ جَمَعَرْ كُوَ سُكَ كَٰوُاْ هَدَايُ دَ ݣَوْتَيْ نَنُونَ غُواْدِيَ؞ وَطَنْدَ ظُكَاتَنْسُ سُكَيِ نِيَّ سُكَ كَٰوُاْ هَدَايُ نَڧُواْنَاوَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Hezekiya kuwa ya amsa ya ce, “Yanzu dai kun tsarkake kanku ga Ubangiji. Sai ku zo kusa ku kawo hadayu da sadakoki na godiya a Haikalin Ubangiji.” Sai taron suka kawo hadayu da sadakoki na godiya, dukan waɗanda suka yi niyya kuwa suka kawo hadayu na ƙonawa.