2 Chronicles 30:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Bisa ga umarnin sarki, sai ’yan aika suka tafi ko’ina a Isra’ila da Yahuda da wasiƙu daga sarki da kuma daga fadawansa, wasiƙar tana cewa, “Mutanen Isra’ila, ku dawo ga Ubangiji Allah na Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, domin yă dawo gare ku, ku da kuka tafi, ku da kuka kuɓuce daga hannun sarakuna Assuriya.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ عُمَرْنِنْ سَرْكِنْ كُوَ عَكَ بَظَ یَنْ كَدَتَݣُونَ كُواْعِنَ عَ إِسْرَٰٓءِيلَ دَ يَهُودَ دَ وَسِيڧُ مَاسُ ثٜىٰوَ «يَا كُو مُتَنٜىٰنْ إِسْرَٰٓءِيلَ، كُكُواْمَ وُرِنْ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نَ إِبْرَٰهِيمْ دَ إِسْحَٰڧَ دَ إِسْرَٰٓءِيلَ، وَتُواْ يَعْڧُوبَ؞ كُكُواْمَ دُواْمِنْ اللَّهْ يَكُواْمَ غَرٜىٰكُ، كُو دَ كُكَ ضَغٜىٰ، وَطَنْدَ كُكَ ڟِيرَا دَغَ حَنُّنْ سَرَاكُنَنْ أَسُّرِيَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai mazanni suka tafi ko'ina da ina a dukan ƙasar Isra'ila da ta Yahuza da wasiƙu daga wurin sarki da sarakunansa, yadda sarki ya umarta. “Ya ku jama'ar Isra'ila, ku komo wurin Ubangiji Allah na Ibrahim, da Ishaku, da Isra'ila domin ya sāke juyowa zuwa ga sauranku, waɗanda kuka kuɓuta daga hannun sarakunan Assuriya.