2 Chronicles 31:10 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
sai Azariya babban firist, daga iyalin Zadok ya amsa, “Tun daga lokacin da mutane suka fara kawo taimakonsu ga haikalin Ubangiji, muna da isashe don abinci da kuma da yawa da za mu rage, domin Ubangiji ya albarkaci mutanensa, saboda haka abin da ya ragu a rumbu yana da yawa.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ أَظَرِيَ بَبَّنْ ڢِرِسْتِ دَغَ غِدَنْ ظَدُواكْ يَأَمْسَ وَ هٜىٰزٜىٰكِيَ يَثٜىٰ «تُنْدَغَ لُواْكَثِنْ دَ مُتَنٜىٰ سُكَ ڢَارَ كَٰوُاْ ݣَوْتَنْسُ أَ غِدَنْ يَهْوٜىٰهْ ، مُنَ سَامُنْ إِسَشّٜىٰنْ أَبِنْدَ ذَامُثِ حَرْ مُبَرِ، غَمَا يَهْوٜىٰهْ يَا أَلْبَرْكَثِ مُتَنٜىٰنْسَ سُواْسَيْ؞ شِيَسَا مُنَدَ ضَغُواْوَرْ كَايَنَّنْ دَيَوَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Azariya, babban firist na gidan Zadok, ya amsa masa, ya ce, “Tun lokacin da suka fara kawo sadakarsu a Haikalin Ubangiji, mun ci mun ƙoshi, abin da ya ragu kuwa yana da yawa, gama Ubangiji ya sa wa jama'arsa albarka, saboda haka abin da ya ragu a rumbu yana da yawa.”