2 Chronicles 32:21 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Ubangiji ya aiki mala’ika, wanda ya karkashe dukan jarumawa da shugabanni da kuma hafsoshi a sansanin sarkin Assuriyawa. Saboda haka sai sarkin Assuriya ya janye zuwa ƙasarsa da kunya. Da ya shiga haikalin Allahnsa, sai waɗansu a cikin ’ya’yansa maza suka yanka shi da takobi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَهْوٜىٰهْ كُوَ يَعَيْكَ دَ مَلاَىِٕكَ يَكَكَّشٜىٰ سُواْجُواْجِ مَاسُ عِيَ يَاڧِ نَ أَسُّرِيَ دَ مَنْيَنْ سُواْجُواْجِنْسُ دَ شُوغَبَنِّنْ سُواْجُواْجِنْسُ عَثِكِنْ سَنْسَنِنْ يَاڧِنْسُ؞ سَبُواْدَ حَكَ سٜىٰنَّكٜىٰرِبْ يَكُواْمَ ڧَسَرْسَ ثِكِنْ ڧَسْڧَنْثِ؞ وَتَرَانَ سَعَدَّ يَنَ سُجَّدَ أَطَاكِنْ اللَّهْ‌نْسَ، سَيْ وَطَنْسُ یَیَنْسَ مَظَا سُكَ كَشٜىٰشِ دَ تَكُواْبِے؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji kuwa ya aiki mala'ika wanda ya karkashe manyan jarumawa, da sarakunan yaƙi, da shugabanni, da kowane riƙaƙƙen soja, da sarkin yaƙi da yake a sansanin Sarkin Assuriya. Sai ya koma ƙasarsa cike da kunya. Sa'ad da ya shiga gidan gunkinsa, sai waɗansu daga cikin 'ya'yan cikinsa suka kashe shi da takobi.