2 Chronicles 33:19 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Addu’arsa da yadda Allah ya taɓu ta wurin tubansa, da kuma dukan zunubansa da rashin biyayyarsa, da wuraren da ya gina masujadan kan tudu ya kuma kafa ginshiƙan Ashera da gumaka kafin ya ƙasƙantar da kansa, duka suna a rubuce cikin tarihin mai duba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَدُّعَرْ سَرْكِے دَ يَدَّ اللَّهْ يَكَرْٻِ ضُواْڧُوانْسَ سُنَ أَرُبُوثٜىٰ عَثِكِنْ لِتَّڢِنْ تَارِيحِنْ مَاسُ غَنِ؞ أَنْ كُمَ رُبُوتَ دُكَنْ ذُنُبَنْسَ دَ رَشِنْ أَمِنْثِنْسَ دَ وُرَارٜىٰنْ سُجَّدَ دَ بَسُ دَاثٜىٰبَ وَطَنْدَ يَغِغِّنَ دَ غُمَكَنْ أَشٜىٰرَ دَ يَكَڢَ دَ غُمَكَنْدَ يَبَوْتَاوَ كَاڢِنْ تُوبَرْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Addu'arsa, da yadda Allah ya karɓi roƙonsa, da dukan zunubinsa, da rashin amincinsa, da wuraren da ya gina masujadai, ya kafa Ashtarot da siffofi, kafin ya ƙasƙantar da kansa, suna nan a rubuce a littafin Hozai.