2 Chronicles 34:33 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Yosiya ya fitar da dukan gumakan banƙyama daga dukan yankunan Isra’ilawa, ya kuma sa dukan waɗanda suke a Isra’ila su bauta wa Ubangiji Allahnsu. Muddin ransa, ba su fasa bin Ubangiji Allah na kakanninsu ba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يُواْسِيَا كُوَ يَكَوَرْدَ دُكَنْ أَبُبُوَنْ بَنْ ڨَمَ دَغَ دُكَنْ ڧَسَرْ إِسْرَٰٓءِيلَ؞ يَكُمَ عُمَرْثِ دُكَنْ وَطَنْدَ سُكٜىٰ ثِكِنْ إِسْرَٰٓءِيلَ سُبَوْتَاوَ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْسُ؞ دُكَنْ ݣُونَكِنْ رَايُوَرْسَ، مُتَنٜىٰ بَسُ جُويَا وَ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نَكَاكَنِّنْسُ بَايَبَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yosiya kuwa ya kawar da dukan abubuwan banƙyama daga dukan ƙasar da jama'ar Isra'ila suke da ita. Ya sa dukan waɗanda suke a Isra'ila su bauta wa Ubangiji Allahnsu. A dukan kwanakin ransa, ba su kauce daga bin Ubangiji Allah na kakanninsu ba.