2 Chronicles 36:17 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya bashe su ga sarkin Babiloniyawa wanda ya karkashe samarinsu da takobi a wuri mai tsarki, bai yi juyayin saurayi, ko budurwa, ko tsoho, ko gajiyayye ba. Allah ya bashe su duka ga Nebukadnezzar.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَبُواْدَ حَكَ يَهْوٜىٰهْ يَسَا سَرْكِنْ بَابِيلَ يَكَٰوُاْ مُسُ يَاڧِ؞ سَرْكِے يَكَكَّشٜىٰ سَمَارِنْ يَهُودَ دَ تَكُواْبِے حَرْ ثِكِنْ غِدَنْ يَهْوٜىٰهْ مَيْ ڟَرْكِے؞ بَيْ جِ تَوْسَيِنْ كُواْوَ بَ، بَبَّ دَ ڧَرَمِ، سَوْرَيِ كُواْ بُدُرْوَ، مَيْ لَاڢِيَ كُواْ مَرَرْ لَاڢِيَ؞ دُكَنْسُ اللَّهْ يَبَاشٜىٰسُ أَ حَنُّنْ سَرْكِنْ بَابِيلَ مُتُمِنْ كَلْدِيَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Don haka Ubangiji ya bashe su ga Sarkin Kaldiyawa wanda ya karkashe samarinsu da takobi a Haikali, bai yi juyayin saurayi, ko budurwa, ko tsoho, ko gajiyayye ba. Allah ya bashe su duka a hannunsa.