2 Chronicles 36:22 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Don a cika maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya, a shekara farko ta Sairus sarkin Farisa, sai Ubangiji ya motsa zuciyar Sairus na Farisa don yă yi shela a dukan masarautarsa, ya kuma sa shi a rubuce cewa,
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَ شٜىٰكَرَا تَڢَرْكُواْ تَمُلْكٍ سَرْكِے سَيِرُسْ نَ ڢَٰشِيَ، سَيْ يَهْوٜىٰهْ يَمُواْڟَ ذُوثِيَارْ سَرْكِے سَيِرُسْ يَعُمَرْتَ عَيِ شٜىٰلَرْ سَڧُواْ عَثِكِنْ دُكَنْ مُلْكِنْسَ؞ وَنَّنْ يَڢَرُ نٜىٰ دُواْمِنْ عَثِكَ مَغَنَرْ يَهْوٜىٰهْ تَبَاكِنْ أَنَّبِے إِرْمِيَ؞ أَنْ كُمَ رُبُوتَ سَڧُوانْ ثٜىٰوَ
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji kuwa ya iza Sairus Sarkin Farisa a shekarar da ya ci sarauta, domin a cika maganar da Ubangiji ya faɗa wa Irmiya. Sai ya yi shela a dukan ƙasar mulkinsa, aka kuma rubuta shelar.