2 Chronicles 6:36 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wani wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su ka miƙa su ga abokin gāba, wanda ya kai su zaman bauta a ƙasa mai nisa ko kuwa kusa;
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«مَيْ يِوُوَ مُتَنٜىٰنْكَ سُكَيِ مَكَ ذُنُوبِ، غَمَا بَ طَنْ أَدَمْ دَ بَايَ ذُنُوبِ، كَكُمَيِ ڢُشِے دَسُو كَبَاشٜىٰسُ أَ حَنُّنْ أَبُواْكَنْ غَابَنْسُ، حَرْ عَكَ ݣُوشٜىٰسُ ذُوَا وَتَ ڧَسَا مَيْ نِيسَ كُواْ كُسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Sa'ad da suka yi maka zunubi (gama ba wani ɗan adam da ba ya yin zunubi), ka kuwa yi fushi da su, har ka bashe su a hannun magabtansu, magabtansu suka kakkama su suka kai wata ƙasa ta nesa ko ta kusa,