2 Chronicles 7:14 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
in mutanena, waɗanda ake kira da sunana, sun ƙasƙantar da kansu, suka kuma yi addu’a, suka nemi fuskata, suka kuma juye daga mugayen hanyoyinsu, zan ji daga sama in kuma gafarta zunubinsu in kuwa warkar da ƙasarsu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عِدَنْ مُتَنٜىٰنَ وَطَنْدَ عَكٜىٰ كِرَنْسُ دَ سُونَنَ سُنْ ڧَسْڧَنْتَرْ دَكَنْسُ، سُنْيِ أَدُّعَ، سُنْ نٜىٰمِ ڢُسْكَتَ، سُنْ جُويُواْ سُنْ بَرْ مُوغَيٜىٰنْ أَيُّكَنْسُ، ذَنْجِے دَغَ سَمَ؞ ذَنْ غَاڢَرْتَ ذُنُوبِنْسُ، إِنْكُمَ وَرْكَرْدَ ڧَسَرْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
in jama'ata waɗanda ake kiransu da sunana za su yi tawali'u, su yi addu'a, su nemi fuskata, su juyo su bar mugayen ayyukansu, sa'an nan sai in ji su daga Sama, in gafarta zunubansu, in kuma warkar da ƙasarsu.