2 Chronicles 8:11 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Solomon ya kawo ’yar Fir’auna daga Birnin Dawuda zuwa fadan da ya gina mata, gama ya ce, “Matata ba za tă zauna a fadan Dawuda sarkin Isra’ila ba, domin wuraren da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga masu tsarki ne.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ سُلَيْمَٰنُ يَكَٰوُاْ یَرْ ڢِرْعَوْنَ دَغَ بِرْنِنْ دَاوُدَ ذُوَا غِدَنْدَ يَغِنَ مَتَ؞ غَمَا يَثٜىٰ «مَاتَتَ بَذَاتَ ذَوْنَ أَ غِدَنْ دَاوُدَ سَرْكِنْ إِسْرَٰٓءِيلَ بَ، غَمَا دُكْ عِنْدَ عَݣُوتِنْ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَرْ يَهْوٜىٰهْ يَكٜىٰ، وُرِے نٜىٰ مَيْ ڟَرْكِے؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sulemanu kuwa ya kawo 'yar Fir'auna daga birnin Dawuda zuwa gidan da ya gina mata, gama ya ce, “Matata ba za ta zauna a gidan Dawuda, Sarkin Isra'ilawa ba, saboda duk wuraren da akwatin Ubangiji ya shiga sun tsarkaka.”