2 Kings 1:16 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Iliya ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah a Isra’ila ne wanda za ka tuntuɓa da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron? Domin ka yi haka, ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ إِلْيَاسُ يَثٜىٰ وَسَرْكِے «إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ، ‹تُنْدَيَكٜىٰ كَعَيْكُواْ دَ یَنْ عَيْكَ ذُوَا وُرِنْ بَعَلْظٜىٰبُبْ اللَّهْنْ عٜىٰكْرُوانْ، كَمَرْ بَابُ اللَّهْ عَ إِسْرَٰٓءِيلَ وَنْدَ ذَاكَ نٜىٰمِ نُڢِنْسَ، تُواْ، بَذَاكَ وَرْكٜىٰ بَ، لَلَّيْ ذَاكَ مُتُ؞› »
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya ce wa sarki, “Ubangiji ya ce, ‘Domin ka aiki manzanni su yi tambaya wurin Ba'alzabul, gunkin Ekron, ba Allah a Isra'ila ne wanda za ka yi tambaya a wurinsa? Domin haka ba za ka sauko daga kan gadon da kake kwance ba, amma za ka mutu lalle.’ ”