2 Kings 1:6 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai suka amsa, “Wani mutum ya sadu da mu ya ce mana, ‘Ku koma wurin sarkin da ya aike ku, ku ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah ne a Isra’ila da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron? Saboda haka ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba. Ba shakka za ka mutu!” ’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سُكَ أَمْسَوَ سَرْكِے سُكَثٜىٰ «وَنِ مُتُمْ يَسَامٜىٰمُ أَ حَنْيَ يَثٜىٰ مَنَ، ‹كُكُواْمَ وُرِنْ سَرْكِنْدَ يَعَيْكٜىٰكُ كُثٜىٰ مَسَ «إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ، شِنْ، بَابُ اللَّهْ نٜىٰ عَ إِسْرَٰٓءِيلَ دَ كُكٜىٰ تَڢِيَ نٜىٰمَنْ أَمْسَ دَغَ بَعَلْظٜىٰبُبْ اللَّهْنْ عٜىٰكْرُوانْ؟ سَبُواْدَ حَكَ بَذَاكَ تَاشِ دَغَ كَنْ غَدُوانْ دَ كَكٜىٰ ݣُونْثٜىٰ بَ، لَلَّيْ ذَاكَ مُتُ؞» › »
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Suka ce masa, “Wani mutum ya sadu da mu, ya ce mana, mu koma wurinka mu shaida maka, ‘Ubangiji ya ce, ba Allah a Isra'ila, har aka aike ku ku tambayi Ba'alzabul, gunkin Ekron? Domin haka ba za ka tashi daga kan gadon da kake kwance ba, amma lalle za ka mutu.’ ”