2 Kings 1:9 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai sarki ya aiki kaftin da sojojin hamsin wurin Iliya. Kaftin ya haura wajen Iliya, wanda yake zaune a kan tudu, ya ce masa, “Mutumin Allah, sarki ya ce, ‘Ka sauko, ka zo!’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ سَرْكِے يَعَيْكَ دَ بَبَّنْ سُواْجَ تَرٜىٰدَ ڧُنْغِيَرْ سُواْجُواْجِ حَمْسِنْ سُجٜىٰ سُكَامَ إِلْيَاسُ؞ بَبَّنْ سُواْجَنْ يَتَڢِے يَسَامٜىٰشِ يَنَ ذَمَ عَكَنْ تُدُ، سَيْيَثٜىٰ مَسَ «يَا مُتُمِنْ اللَّهْ ، سَرْكِے يَثٜىٰ كَسَوْكَ ڧَسَا؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan sarki ya aiki shugaba tare da mutum hamsin su taho da Iliya. Mutumin kuwa ya haura wurin Iliya a kan dutse, ya ce masa, “Ya mutumin Allah, sarki ya umarta ka sauko.”