2 Kings 10:21 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan ya aika saƙo ko’ina a Isra’ila, dukan masu yi wa Ba’al hidima kuwa suka tattaru, ba mutumin da bai zo ba. Suka yi cincirindo a haikalin Ba’al har sai da ya cika makil.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يٜىٰهُو يَعَيْكَ دَ سَڧُواْ ذُوَا كُواْعِنَ عَڧَسَرْ إِسْرَٰٓءِيلَ يَغَيَّثِ دُكَنْ مَاسُ سُجَّدَ غَ بَعَلْ سُذُواْ؞ دُكَنْسُ سُكَذُواْ، بَاوَنْدَ يَڢَسَ ذُوَا، حَرْ سُكَ ثِكَ غِدَنْ بَعَلْ مَڧِلْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
sai ya aika cikin Isra'ila duka, dukan masu yi wa Ba'al sujada kuwa suka zo, ba wanda bai zo ba. Suka shiga, suka cika haikalin Ba'al makil daga wannan gefe zuwa wancan.