2 Kings 13:14 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَدَّ أَلْيَسَعَ يَكَمُ دَ رَشِنْ لَاڢِيَرْ دَ ذَيْ كَيْ غَ مُتُوَ، سَرْكِے يٜىٰهُواْوَشْ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ يَغَنْغَرَ ذُوَا وُرِنْسَ، يَيِ كُوكَا أَغَبَنْسَ يَنَ ثٜىٰوَ «بَابَنَ! بَابَنَ! كَيْ مَيْ ڟَرٜىٰ إِسْرَٰٓءِيلَ ڢِيٜىٰدَ كٜىٰكُنَنْ دُواْكِنْتَ دَ سُواْجُواْجِنْتَ!»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da Elisha ya kamu da ciwon ajali, sai Yehowash Sarkin Isra'ila ya tafi wurinsa, ya yi kuka a gabansa, yana cewa, “Ubana, Ubana, karusar Isra'ila da mahayan dawakanta!”