2 Kings 15:16 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A lokacin nan sai Menahem ya taso daga Tirza, ya kai wa Tifsa hari da kowa wanda yake a birnin da kewayenta, don sun ƙi su buɗe ƙofofinsu. Ya kori Tifsa daga aiki, ya kuma tsattsaga cikin dukan mata masu juna biyu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَ لُواْكَثِنْ دَ مٜىٰنَهٜىٰمْ يَكٜىٰ هَوْرُواْوَ دَغَ تِرْظَ، يَذُواْ يَهَلَّكَ غَرِنْ تِڢْسَ دَ مُتَنٜىٰنْ غَرِنْ، تَرٜىٰدَ ڧَوْيُكَنْ دَسُكٜىٰ كٜىٰوَيٜىٰ دَشِ، غَمَا مُتَنٜىٰنْ غَرِنْ سُنْڧِے سُكَرْٻٜىٰشِ؞ حَرْ مَا مَاتَا مَاسُ جُونَ بِيُ يَڟَڟَّٰغٜىٰ ثِكِنْسُ؞ ﴿شٜىٰكَرَا 743-738 كَاڢِنْ حَيْڢُوَرْ عِيسَىٰ ﴾
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A lokacin nan sai Menahem ya hallaka Tifsa da dukan waɗanda suke cikinta, da karkararta tun daga Tirza, domin ba su karɓe shi ba, saboda haka ya hallaka ta, ya tsattsage dukan matan da suke da juna biyu.