2 Kings 15:25 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ɗaya daga cikin manyan fadawansa, Feka ɗan Remaliya, ya ƙulla masa maƙarƙashiya. Ɗauke da mutanen Gileyad hamsin, ya kashe Fekahiya tare da Argob da kuma Ariye a fadan sarki a Samariya. Ta haka Feka ya kashe Fekahiya ya kuma gāje shi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ شُوغَبَنْ سُواْجُواْجِنْسَ ڢٜىٰكَ طَنْ رٜىٰمَلِيَ، يَيِ ڧُلّٜىٰ ڧُلّٜىٰنْ كَشٜىٰشِ تَرٜىٰدَ مُتَنٜىٰ حَمْسِنْ دَغَ غِلٜىٰيَدْ؞ سُكَ كُوَ كَشٜىٰشِ أَوُرِے مَيْ كَتَنْ‌غَ نَغِدَنْ سَرْكِے أَ سَمَرِيَ تَرٜىٰدَ أَرْغُوابْ دَ أَرِيٜىٰ؞ تَهَكَ ڢٜىٰكَ يَهَوْ كُجٜىٰرَرْ مُلْكٍ ڢٜىٰكَهِيَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai shugaban sojojinsa, wato Feka, ɗan Remaliya daga Gileyad, tare da mutum hamsin suka ƙulla maƙarƙashiya, suka kashe Fekahiya tare da Argob da Ariye a Samariya a fādarsa. Da suka kashe shi, sai Feka ya zama sarki.