2 Kings 15:29 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A zamanin Feka sarkin Isra’ila, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo ya kama Iyon, Abel-Bet-Ma’aka, Yanowa da Kedesh da kuma Hazor. Ya kame Gileyad da Galili, haɗe da dukan ƙasar Naftali, ya kuma kwashi mutanen zuwa Assuriya.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَ لُواْكَثِنْ مُلْكٍ سَرْكِے ڢٜىٰكَ نَ إِسْرَٰٓءِيلَ، سَرْكِے تِغْلَتْ ڢِلٜىٰسٜىٰرْ نَ أَسُّرِيَ يَذُواْ يَڨُوثٜىٰ غَرِنْ إِيُوانْ دَ أَبٜىٰلْ بٜىٰتْ مَعَكَ دَ يَنُواْوَ دَ كٜىٰدٜىٰشْ دَ حَزُوارْ دَ غِلٜىٰيَدْ دَ غَلِيلِ دَ دُكَنْ يَنْكِنْ ڧَسَرْ نَڢْتَلِ؞ يَكُمَ ݣُوشِ مُتَنٜىٰ ذُوَا بَوْتَا أَعَسُّرِيَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A zamanin Feka Sarkin Isra'ila, sai Tiglat-filesar mai mulkin Assuriya, ya zo ya ci Iyon, da Abel-bet-ma'aka, da Yanowa, da Kedesh, da Hazor, da Gileyad, da Galili, da dukan ƙasar Naftali. Sa'an nan ya kwashe mutane zuwa bauta a Assuriya.