2 Kings 17:13 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ubangiji ya yi wa Isra’ila da Yahuda kashedi ta bakin dukan annabawansa da kuma masu duba, cewa, “Ku juyo daga mugayen ayyukanku. Ku yi biyayya da umarnai da farillaina, bisa ga dukan Dokar da na dokaci kakanninku su bi, waɗanda na kuma bayar ta wurin bayina, annabawa.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كُلُّمْ يَهْوٜىٰهْ يَايِ تَغَرْغَطِے إِسْرَٰٓءِيلَ دَ يَهُودَ تَبَاكِنْ كُواْوَنٜىٰ أَنَّبِے دَ كُواْوَنٜىٰ مَيْ غَنِ ثٜىٰوَ «كُجُويَا دَغَ مُوغَيٜىٰنْ هَنْيُواْيِنْكُ! كُكِيَايٜىٰ عُمَرْنَيْنَ دَ ڧَٰعِدُواْدِنَ بِسَغَ كُواْيَرْوَاتَا، وَدَّ نَعُمَرْثِ كَاكَنِّنْكُ، وَدَّ كُمَ نَعَيْكَ مُكُ تَبَاكِنْ بَايِنَ أَنَّبَاوَا؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Amma Ubangiji ya faɗakar da jama'ar Isra'ila da jama'ar Yahuza ta bakin annabawa da kowane maigani, cewa su bar mugayen hanyoyinsu, su kiyaye umarnansa da dukan dokokinsa waɗanda ya umarci kakanninsu da su, waɗanda kuma ya aiko musu ta wurin bayinsa annabawa.