2 Kings 18:14 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Hezekiya sarkin Yahuda ya aika saƙo ga sarkin Assuriya a Lakish cewa, “Na yi laifi, ka janye daga gare ni, zan kuma biya ka duk abin da ake bukata daga gare ni.” Sarkin Assuriya ya karɓi talenti ɗari uku na azurfa, da talenti talatin na zinariya daga hannun Hezekiya sarkin Yahuda.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ سَرْكِے هٜىٰزٜىٰكِيَ يَعَيْكَ دَ سَڧُواْ غَ سَرْكِنْ أَسُّرِيَ عَبِرْنِنْ لَكِشْ ثٜىٰوَ «نَيِ لَيْڢِے، بَرِ كَجَنْيٜىٰ سُواْجُواْجِنْكَ، كَبَرْنِ؞ دُكْ أَبِنْدَ كَثٜىٰ مِنِ ذَنْ بِيَ؞» سَعَنً سَرْكِنْ أَسُّرِيَ يَسَا هٜىٰزٜىٰكِيَ يَعَيْكُواْ مَسَ دَ كِلُواْ دُبُو غُواْمَ نَأَظُرْڢَا دَ كِلُواْ دُبُو طَيَ نَظِينَارِيَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Hezekiya, Sarkin Yahuza, ya aika zuwa wurin Sarkin Assuriya a Lakish cewa, “Na yi laifi, ka ƙyale ni, duk abin da ka ɗora mini zan ɗauka.” Sai Sarkin Assuriya ya ce wa Hezekiya Sarkin Yahuza ya ba shi talanti ɗari uku na azurfa, da talanti talatin na zinariya.