2 Kings 19:35 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A daren nan mala’ikan Ubangiji ya fita ya kashe dakaru dubu ɗari da tamanin da biyu a sansanin Assuriyawa. Da mutane suka farka da safe, sai ga gawawwaki ko’ina.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَ دَرٜىٰنَّنْ مَلاَىِٕكَنْ يَهْوٜىٰهْ يَتَڢِے وُرِنْ سَنْسَنِنْ يَاڧِنْ أَسُّرِيَ يَكَشٜىٰ مُتُمْ دُبُو طَرِے دَ دُبُو تَمَٰنِنْ دَ بِيَرْ؞ وَشٜىٰغَرِ دَ عَكَ تَاشِ، سَيْغَا غَوَوَّكِ كُواْعِنَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A daren nan, sai mala'ikan Ubangiji ya tafi ya kashe Assuriyawa a sansaninsu, mutum dubu ɗari da dubu tamanin da dubu biyar (185,000). Sa'ad da mutanen Isra'ila suka tashi da sassafe, sai suka ga gawawwakin nan kwance.