2 Kings 2:16 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Suka ce, “Duba, mu bayinka muna da masu ji da ƙarfi hamsin. Bari su je su nemi maigidanka. Wataƙila, Ruhun Ubangiji ya ɗauke shi ya ajiye bisa wani dutse, ko wani kwari.” Elisha ya ce, “A’a, kada ku aike su.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سُكَثٜىٰ مَسَ «غَاشِ، أَݣَويْ مَظَا حَمْسِنْ مَاسُ ڧَرْڢِے عَثِكِنْ بَايِنْكَ؞ كَيَرْدَ مُسُ سُتَڢِے سُنٜىٰمِ شُوغَبَنْكَ؞ وَتَڧِيلَ رُوحٌ يَهْوٜىٰهْ يَطَوْكٜىٰشِ يَكَيْشِ كَنْ وَنِ بَبَّنْ تُدُ كُواْ ثِكِنْ وَنِ ݣُورِ؞» عَمَّا أَلْيَسَعَ يَأَمْسَ يَثٜىٰ «أَعَ، كَدَكُ عَيْكٜىٰسُ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
suka kuma ce masa, “Yanzu fa, ga mu mu hamsin ƙarfafa. Bari mu tafi mu nemo maigidanka, mai yiwuwa ne Ruhun Ubangiji ya ɗauke shi, ya jefa shi kan wani dutse, ko cikin wani kwari.” Elisha ya ce, “Kada ku tafi.”