2 Kings 2:8 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Iliya ya tuɓe rigarsa, ya nannaɗe ya bugi ruwan Urdun da shi. Sai ruwan ya dāre gida biyu, suka haye a busasshiyar ƙasa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ إِلْيَاسُ يَثِرٜىٰ بَبَّرْ رِغَرْسَ يَنَنَّطٜىٰتَ يَبُغِ ضُوً كُواْغِنْ دَ عِتَ؞ سَيْ ضُوً يَرَبُ كَشِ بِيُ، سَيْ شِ دَ أَلْيَسَعَ سُكَ ڧٜىٰتَرٜىٰ كُواْغِنْ عَبُوسَشِّيَرْ ڧَسَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan Iliya ya tuɓe alkyabbarsa, ya naɗe ta, ya bugi ruwa da ita, sai ruwan ya dāre, ya rabu biyu, dukansu biyu fa suka taka sandararriyar ƙasa suka haye.